Gwamnatin ta bayarada wannan sanarwa yayin taron ministocin ta na makon jiya kuma yankunan nemen ma'adunan da suka hada da zinare, azurfa, gawayi da dai sauran su a jihohin Tillabery dake yammacin kasar, da jihar Tawa dake tsakiya da kuma Agades dake Arewacin kasar. A cikin yajejenoyoyin da gwamnatin ta sa hannu da wadanan kanfanonin an kiyasta kasar zata anfana da kudade da yawan su ya kai sama da milliyan 35 na dallar Amurka a shekara uku masu zuwa. Baya ga dai wadanan ma'adunan Allah ya albarkaci Nijar da arzikin kashen Urenium wace ake hasashen a shekaru masu zuwa zata kasance ta uku a duniya wajen arzikin uranium, to saidai duk kwa da wannan kasar na zamen kura baya cikin kasahen mafi talaici a Duniya. ABNA
14 Oktoba 2014 - 15:17
Lambar labari: 644311
A cikin wani tsarin ta na ci gaban fannin ma'adunai, Gwamanatin Nijar ta sanarda raraba wasu lasisin neman ma'adunai karkashin kasa ga wasu kanfanonin ciki da wajen kasar 12.